Majalisa ta yi sammacin kwamishanan Nasarawa

Majalisar dokokin jihar Nasarawa tayi sammacin kwamishinan muhalli da albarkatun kasa, Yakubu Kwanta, domin ya bayyana a gaban majalisar a ranar Litinin, 16 ga Disamba, 2024, bisa tuhumar rashin biyayya.

Majalisar dai ta sha alwashin daukar tsatstsauran mataki kansa muddin ya gaza bayyana a gabanta.

Shugaban Majalisar, Danladi Jatau, ya bayar da wannan umarnin lokacin da shugaban kwamitin Majalisar kan Gidaje da Muhalli, wanda kuma ke wakiltar mazabar Keana, Muhammad Adamu Omadefu, ya gabatar da batun yayin zaman Majalisar a Lafiya, babban birnin jihar a jiya Alhamis.

Kwamishinan zai bayyana ne domin kare kasafin kudin ma’ikatar sa, a kasafin kudin 2025 da gwamnan ya gabatar.

Shugaba majalisar ya bayyana cewa ba za su lamunci kowanne irin rashin biyayya daga kowanne kwamishina a jihar ba.

Tags:

Recent News

Kenyan police block access to Nairobi city centre ahead of planned government protests

Nairobi Police Block Roads and Disperse Crowds as Anti-Government Protests Erupt Over Corruption and Brutality

Tinubu urges reforms, more inclusion for Africa — Daily Nigerian

Tinubu Calls for Global Reforms at BRICS Summit

Put safely measures in place to prevent incessant inferno - Olubadan tells market leaders

Olubobadan of Ibadanland Oba Owolabi Olakulehin Dies at 90

Scroll to Top