Majalisa ta yi sammacin kwamishanan Nasarawa

Majalisar dokokin jihar Nasarawa tayi sammacin kwamishinan muhalli da albarkatun kasa, Yakubu Kwanta, domin ya bayyana a gaban majalisar a ranar Litinin, 16 ga Disamba, 2024, bisa tuhumar rashin biyayya.

Majalisar dai ta sha alwashin daukar tsatstsauran mataki kansa muddin ya gaza bayyana a gabanta.

Shugaban Majalisar, Danladi Jatau, ya bayar da wannan umarnin lokacin da shugaban kwamitin Majalisar kan Gidaje da Muhalli, wanda kuma ke wakiltar mazabar Keana, Muhammad Adamu Omadefu, ya gabatar da batun yayin zaman Majalisar a Lafiya, babban birnin jihar a jiya Alhamis.

Kwamishinan zai bayyana ne domin kare kasafin kudin ma’ikatar sa, a kasafin kudin 2025 da gwamnan ya gabatar.

Shugaba majalisar ya bayyana cewa ba za su lamunci kowanne irin rashin biyayya daga kowanne kwamishina a jihar ba.

You may also like

Recent News

AFCON 2025: Super Eagles give injury update on Ndidi, AlebiosuĀ 

Manchester United eye Wilfred Ndidi transfer move

How audit report exposed massive financial irregularities in Kano ministries, KASCO — Daily Nigerian

Kano financial audit reveals massive irregularities and abuse

Atiku, Tambuwal destroyed PDP - Fayose

Fayose Reveals Details of Makinde’s Meeting with Tinubu

Flutterwave partners with Turnkey to power secure stablecoin wallets for customers

Stablecoin payments launched by Flutterwave for African merchants

Scroll to Top