Majalisa ta yi sammacin kwamishanan Nasarawa

Majalisar dokokin jihar Nasarawa tayi sammacin kwamishinan muhalli da albarkatun kasa, Yakubu Kwanta, domin ya bayyana a gaban majalisar a ranar Litinin, 16 ga Disamba, 2024, bisa tuhumar rashin biyayya.

Majalisar dai ta sha alwashin daukar tsatstsauran mataki kansa muddin ya gaza bayyana a gabanta.

Shugaban Majalisar, Danladi Jatau, ya bayar da wannan umarnin lokacin da shugaban kwamitin Majalisar kan Gidaje da Muhalli, wanda kuma ke wakiltar mazabar Keana, Muhammad Adamu Omadefu, ya gabatar da batun yayin zaman Majalisar a Lafiya, babban birnin jihar a jiya Alhamis.

Kwamishinan zai bayyana ne domin kare kasafin kudin ma’ikatar sa, a kasafin kudin 2025 da gwamnan ya gabatar.

Shugaba majalisar ya bayyana cewa ba za su lamunci kowanne irin rashin biyayya daga kowanne kwamishina a jihar ba.

You may also like

Recent News

PRP woos Atiku, Obi, Kwankwaso, others to rescue Nigeria — Daily Nigerian

PRP Urges Opposition Leaders To Unite Amid ADC Crisis

APC now desperate, Tinubu doesn't want elections in 2027 - Dino Melaye

Melaye Claims APC Panics Over Rising ADC Defections

media talk africa default image logo

Zimbabwe Gender Commission Abolition Alarms Survivors

Flutterwave announces banking license, to rival Nigerian banks

Flutterwave Receives Full CBN Banking License Today

Scroll to Top