Majalisa ta yi sammacin kwamishanan Nasarawa

Majalisar dokokin jihar Nasarawa tayi sammacin kwamishinan muhalli da albarkatun kasa, Yakubu Kwanta, domin ya bayyana a gaban majalisar a ranar Litinin, 16 ga Disamba, 2024, bisa tuhumar rashin biyayya.

Majalisar dai ta sha alwashin daukar tsatstsauran mataki kansa muddin ya gaza bayyana a gabanta.

Shugaban Majalisar, Danladi Jatau, ya bayar da wannan umarnin lokacin da shugaban kwamitin Majalisar kan Gidaje da Muhalli, wanda kuma ke wakiltar mazabar Keana, Muhammad Adamu Omadefu, ya gabatar da batun yayin zaman Majalisar a Lafiya, babban birnin jihar a jiya Alhamis.

Kwamishinan zai bayyana ne domin kare kasafin kudin ma’ikatar sa, a kasafin kudin 2025 da gwamnan ya gabatar.

Shugaba majalisar ya bayyana cewa ba za su lamunci kowanne irin rashin biyayya daga kowanne kwamishina a jihar ba.

You may also like

Recent News

Dangote Refinery failed to meet domestic supply target — NMDPRA

Dangote Refinery faces capacity challenge amid RFCC shutdown

Dangote Cement Hires 200 Graduates In Fresh Boost To Local Content • Channels Television

Dangote Cement inducts 200 new engineers and professionals

'I can’t walk alone in my estate, strange men follow me’ – Actress Teniola Aladese

Nollywood star shares safety concerns in Lekki estate

Nigeria records first robotic gynaecological surgery in West Africa — Daily Nigerian

Robotic surgery milestone achieved in Nigeria

Scroll to Top